Connect with us

Labarai

INEC ta gargadi masu yunkurin kawo mata cikas a zaben gwamnan Anmabra

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta gargadi mutanen dake yunkurin gurgunta shirin ta na gudanar da sahihin zaben gwamnan jihar Anmabra da za’a gudanar ranar Asabar mai zuwa 8 ga wannan watan Nuwamba.

A cewar shugaban hukumar Farfesa Joash Amupitan sun shirya tsaf don tabbatar da zaben kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar nan ya sahale.

A wata sanarwa da sakataran yada labaran shugaban hukumar Dayo Oketola ya fitar ya ce shugaban hukumar ya bayyana dukkan masu ruwa da tsaki tabbacin yin zabe mai cike da tsafta cikin tsarin gudanarwa.

Haka kuma ya bukaci masu ruwa da tsakin jihar dasu kasance masu aiki tare, kamar yadda aka samar da cikakken tsarin tsaro kafin da ya yin da kuma bayan kammala zaben.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!