Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

INEC SOKOTO:Gwamna Tambuwal ya ce basu amince da ayyana zaben jihar bai kammala ba

Published

on

Gwamnan jihar Sakkwato kuma dan takarar gwamnan jahar a karkashin jam’iyyar PDP, Alhaji Aminu Waziri Tambuwal, ya ce basu amince da ayyana zabe a matsayin wanda bai kammala ba.

Gwamnan na wadannan kalamai ne yayin taron gaggawa da manema labarai da suka gudanar tare da masu ruwa da tsaki a jihar da yammacin jiya Litnin.

Gwamna Tambuwal ya ce sun yi natsarin kundin tsarin mulkin kasa da na hukumar zabe amma basu ga inda aka bayyana wannan dokar da ta ce a ayyana wani zabe a matsayin wanda bai kammala ba.

Gwamna Tambuwal ya amsa cewa akwai dalilan da kan sa a soke zabe ta yadda ma ba za a sake yi ba; akwai kuma dalilan da kan sa a soke amma kuma a sake wani sabo. Ya ce to amma hukumar INEC ba ta alakanta daya daga cikin irin wadannan yanayi da ayyana zaben jahar Sokoto a matsayin mara kammala da ta yi ba.

Gwamna Tambuwal ya ce ta na yiwuwa su ruga kotu su kalubalanci ayyana zaben a matsayin mara kammala. Ya kuma yi nuni da cewa akasarin jahohin da aka ayyana zabensu a matsayin marasa kammala ‘yan takarar PDP ne ke kan gaba. Sannan ya yi hanunka mai sanda ga jami’an hukumar INEC da cewa idon duniya na kansu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!