Connect with us

Labarai

Jami’an tsaro na daukar matakai kan sake bullar yan Achaba- Kwamishina Waiya

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta ce hukumomin tsaro sun soma daukar matakai kan sake bullar ayyukan Achaba a sassa da dama na birnin Kano da kuma wasu yankuna da ke kan iyakar jihar, duk da an haramta sanaʼar tsawon lokaci.

Wannan  na cikin sanarwar da Kwamishinan yaɗa labarai Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar a daren ranar Lahadi.

Sanarwar ta bayyana cewa sahihan bayanai sun nuna cewa, yawaitar masu amfani da babura wajen ɗaukar fasinja a unguwanni daban-daban, tare da samun rahoton wasu da ba a san su ba da ke shiga yankuna suna aiki a matsayin ƴan Achaba. 

Ta ce gwamnati ta umurci hukumomin tsaro su karfafa matakan da suke dauka a dukkan kananan hukumomi 44 na jihar.

Sanarwar ta ce gwamnati ta ci gaba da bai wa hukumomin tsaro dukkan goyon bayan da ake bukata, tare da nazarin shawarwarin da jama’a suka bayar kan kara sa ido, musamman a hanyoyin shiga da fita daga Kano domin dakile lamarin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!