Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jami’an tsaro ne suka tilasta min na amsa laifin kashe Hanifa – Abdulmalik Tanko

Published

on

Malamin makarantar nan Abdulmalik Tanko da ake zargi da kashe dalibarsa Hanifa Abubakar ya ce, jami’an tsaro ne suka tursasashi ya amsa laifin da ake zarginsa.

Abdulmalik Tanko ya bayyana hakan a ranar Alhamis a gaban babbar kotun jiha Mai Lanba 5 dake sakatariyar Audu Bako Karkashin jagorancin mai Sharia mai Sharia Usman Na Abba.

A zaman kotun masu gabatar da kara sun ci gaba da gabatar da shaidu inda aka gabatar da jami’an tsaro daga sashin yaki da garkuwa da mutane kuma suka bada shaida.

Inda suka bayyana cewar sunyi musu tambayoyi batare da tursasamusu ba haka Kuma shima Abdulmalik Tanko ya bada bayaninsa inda ya bayyanawa kotu cewar shifa tilasata Masa akayi ya bada bayanansa a wancan lokaci.

Bayan kammala jin nasa bayanin itama Fatima Musa tace ganin abinda ya faru ga su Abdulmalik shi ne ya tsorata ta bada nata bayanin.

Daga karshe kotu taji bayanin kowane bangare bayanda Mai gabatar da Kara kwamishinan Sharia Barisata Musa Abdullahi Lawal yayi masa tambayar cewar duk bayanin daya fada a wajan bincike hakane? sai Yace haka ne.

Kotun ta dage ci gaba da zaman zuwa ranar 9 da 10 ga watan Maris na 2022  domin yin nazarin kotun.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!