Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta wanke matar Abdulmalik Tanko daga zargin kisan Hanifa

Published

on

Wata kotu a nan Kano ta sallami Jamila Muhammad Sani matar Abdulmalik Tanko wanda ake zargi da kashe ɗalibarsa Hanifah Abubakar.

Kotun Majistare mai Lanba 12 ƙarƙashin mai shari’a Muhammad Jibril ta wanke Jamila a zaman kotun na ranar Juma’a kan zargin da ake mata na ɓoyewa Hanifa.

Jami’an tsaro ne suka tilasta min na amsa laifin kashe Hanifa – Abdulmalik Tanko

Tun da fari dai Lauyan gwamnati Barista Lamiɗo Soran ɗinki ne Lauya mai gabatar da ƙara, kuma kotun ta yi la’akari da bayanan da Jamila ta bayar tare da yin nazari inda ta gano bata da wani laifi a kan batun sace Hanifa Abubakar da kuma kasheta.

Wakilin Freedom Radio ta rawaito cewa Jamila tana cike da farin ciki sakamakon wanke ta da kotun ta yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!