Connect with us

Labarai

Jami’anmu na musamman za su sauka a Saudiyya yau- NAHCON

Published

on

Hukumar kula da aikin Hajji ta Najeriya NAHCON, ta ce, a yau Litinin ne tawagarta ta musamman za ta isa kasar Saudiyya domin fara gudanar da shirye-shiryen aikin Hajjin bana.

A cewar ta tsaikon tafiyar ta su da aka samu ya biyo bayan wasu gyare-gyare da ta yi da zai kara samar da ci gaba a aikin hajjin na bana.

Hakan na cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafukanta na Internet kan jinkirin tafiyar da aka samu.

Idan za a iya tunawa dai, a baya shugaban hukumar ta NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana cewa a ranar 30 ga watan Afrilun da ya gabata ne Likitoci da masu kula da alhazai na musamman za su tafi kasar ta Saudiyya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!