Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jami’ar Yusuf Maitama Sule zata fara Post UTME

Published

on

Jami’ar Yusuf Maitama Sule ta sanar da cewa za ta fara aikin rajistar sabbin daliban da za ta tantance domin ba su gurbin karatu wato Post UTME a ranar laraba mai zuwa 26 ga wannan wata na Agusta da muke ciki.

Za a kammala aikin tantancewar a ranar 7 ga watan Oktoba mai zuwa, wato bayan shafe tsawo makonni 6 ana aikin, domin fara shekarar karatu ta 2020 zuwa 2021.

Wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai rikon mukamin magatakar jami’ar Malam Sulaiman Saleh, ta ce tuni aka fitar da adadin makin din da aka kayyade wa ko wane kwas da jami’ar take gudanarwa, kuma ta wallafa shi a shafinta na intanet www.nwu.edu.ng.

Sanarwar ta kara da cewa iya wadanda suke zabi jami’ar a matsayin gurbin farko wato first choice kadai za a baiwa damar yin rajistar domin shiga tantancewar.

 

 

 

 

 

AMA

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!