Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Jam’iyyar APC ta kafa kwamiti na babban taronta mai zuwa ranar Lahadi

Published

on

Jam’iyya mai mulkin na kasa ta APC ta kafa wani Kwamiti mai kunshe da mambobi 68, domin babban taronta, kammar yadda Sakatariyar Jam’iyyar da ke Abuja ta sanar a jiya Lahadi.

Sanarwar ta ayyana gwamnan Jihar Muhammad Badaru a matsayin shugaban kwamitin sai gwamnan Jiar Ondo Rotimi Akeredolu a matsayin mataimakinsa, yayin da Sanata Ben Uwajomogu zai kasance Sakatare kuma Mamba.

Cikin Mambobin kwamitin akwai gwamnoni 10 da wasu ‘yan Majalisun Dokokin kasar nan da kuma manyan jagororin Jam’iyyar.

Gwamnonin sune Rochas Okorocha na Imo da Kashim Shettima na Borno da Aminu Bello Masari na Katsina, sai Abiola Ajimobi na Oyo da Ibrahim Gaidam na Yobe da kuma Nasir El-Rufa’i na Kaduna.

Sauran sun hadar da Simon Lalong na Filato da Bindo Jibrila na Adamawa da Yahaya Bello na Kogi, sai kuma Godwin Obaseki na Jihar Edo, yayin da tsohon shugaban majalisar Dattijai Sanata Ken Nnamani shi ma ya kasance mamba.

‘Yan majalisar dattijan da ke cikin kwamitin su ne Sanata Ahmad Yarima da Adamu Aliero da Danjuma Goje da Abdullahi Adamu, sai George Akume da Ovie Omo-Agege da Andrew Uchendu, sauran su ne Abdullahi Danbaba da Baba Kuka da kuma John Enoch.

Ministoci biyu na cikin kwamitin sun hadar da na Kwadago da nagartar aiki Chris Ngige da takwaransa Neja-Delta Uguru Usani.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!