Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin Kaduna ta bullo da binciken gida-gida don kare al’umma daga kamuwa da cutuka masu yaduwa

Published

on

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bullo da wani tsari na gudanar binciken gida-gida domin kare al’ummarta daga kamuwa daga cutuka masu yaduwa a Jihar da ma makwabtanta.

Kwamishinan Lafiya na Jihar Dokta Paul Dogo ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai jiya a Kaduna, a kokarin kare yaduwar cutuka irin su Kwalara da Sankarau da Kyanda da makamantansu.

Dokta Paul Dogo ya ce ya zuwa yanzu ba su samu labarin bullar ko wace irin cuta ba a cikin kananan hukumomi 23 na Jihar, sannan ya bada tabbacin kare aukuwar barkewar cututtuka a Jihar.

Kamishinan ya tabbatar da cewa sun tanadi magunguna domin rarrabawa Asibitoci da zarar an samu bullar wata cuta a Jihar ciki har da maganin Tarin fuka.

Har ila yau, ya kar da cewa tun daga watan Nuwamban shekarar 2012 ba samu bullar cutar Polio a Jihar ba, a don haka ma suka ci gaba da daukar matakan kariya.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!