Connect with us

Labarai

Jam’iyyar SDP ta kori El-Rufai daga zama a cikinta

Published

on

Jam’iyyar SDP ta kori tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, inda ta bayyana cewa ba zai iya shiga jam’iyyar ba a kowane matsayi na tsawon shekaru 30 masu zuwa.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran SDP na ƙasa Araba Aiyenigba ya fitar a Abuja, jam’iyyar ta ce, El-Rufai bai taɓa yin rajista da jam’iyyar ba a hukumance ba a matakin mazaɓa kamar yadda kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya tanada.

Aiyenigba ya ce, duk da haka, tsohon gwamnan ya fito fili ya yi ikirarin zama memba a shafukan sada zumunta da kuma “takardun jabu” don goyon bayan ikirarin nasa.

Jam’iyyar ta kuma yi zargin cewa ya haɗa kai da jam’iyyar ADC tare da neman janyo jam’iyyar SDP cikin kawancen siyasa mara izini.

SDP ta bukaci hukumar zabe mai zaman kanta INEC da sauran hukumomin da abun ya shafa da kada su amince da El-Rufai a matsayin mamba.

Jam’iyyar SDP ta ce, tsohon gwamnan na Kaduna ba shi da hurumin wakilci ko yin magana a jam’iyyar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!