Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Janar Abdulsalami Abubakar: yan Najeriya su kauracewa abinda zai kawo nakasu ga mulkin demokradiya

Published

on

Kwamitin sasanta ‘yan takarar shugabancin kasar nan da tsohon shugaban mulkin soji Janar Abdussalami Abubakar mai ritaya ke jagoranta; ya bukaci al’ummar Najeriya da su guji aikata wani abu da ka iya janyo nakasu ga dorewar mulkin dimukuradiyar kasar nan.

Kwamitin ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da su mai da batun dage zabukan kasa da hukumar zabe kasa ta INEC ta yi a matsayin wani mataki da ya zama dole, a don haka ya bukace su da su kasance masu kishin kasa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin Janar Abdussalami Abubakar da mai masaukin taron kwamitin Bishop Mathew Hassan Kukah.

A cewar sanawar, kwamitin yana sane da cewa al’ummar kasar nan ba su ji dadin halin da suka tsinci kansu ba sakamakon sauya lokacin gudanar da zaben, sai dai sun ce yana da kyau al’ummar Najeriya su dauki lamarin a matsayin kaddara.

Ta cikin sanarwar da kwamitin ya fitar dai ya kuma ce kamata ya yi al’ummar kasar nan su rika tunanin gaba maimakon waiwayen abinda ya faru a baya domin daukan darasi.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!