Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Jiragen yaki na dakarun Operation Hadarin Daji sun kashe ‘yan bindiga

Published

on

Jiragen yaki na dakarun Operation Hadarin Daji na rundunar sojin kasar nan sun kashe ‘yan bindiga da dama a jihar Zamara.

Bayanai sun tabbatar da cewa jiragen yakin sun kuma lalata maboyar ‘yan bindigara dajin Doumborou da ke jihar ta Zamfara.

Rahotanni sun ce maboyar ‘yan bindigar da jiragen yakin suka lalata suna karkashin kulawar wani gawurtaccen dan ta’adda ne da akewa lakabi da Dangote.

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun shalkwatar tsaro ta kasa manjo janar John Enenche, ta ce a baya-bayan nan ne dakarun suka samu bayanan sirri game da maboyar ‘yan  bindigar a cikin dajin lamarin da ba tare da bata lokaci ba suka kai musu hari ta sama.

Sanarwar ta kuma ruwaito manjo janar John Enenche na cewa dakarun na operation Hadarin Daji za su ci gaba da shiga lunguna da sakuna na dazukan da ke yankin don kakkabe ‘yan ta’adda.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!