Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kaduna: rundunar yan sanda ta Kama wani da ake zargin yana da hannu a kashe basaraken Adara

Published

on

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kaduna ta kama wani mutum da ake zargi yana da hannu a kashe basaraken kasar Adara Maiwada Galadima a kwanakin baya, a jihar ta Kaduna.

 

A dai watan Oktobar shekarar da ta gabata ne aka kashe basaraken kasar ta Adara Maiwada Galadima akan hanyar sa ta dawowa gida, bayan ya raka gwamna Nasir El-rufai zuwa kasuwar Magani don yin jaje ga wadanda rikicin yankin ya shafa.

 

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai Magana da yawun rundunar ‘yan sandan kasar nan DCP Frank Mba.

 

Sanarwar ta ce, mutumin mai suna Abubakar Ibrahim da akewa lakabi da Dan Habu mai shekaru talatin da bakwai, dan asalin yankin karamar hukumar Igabi ne da ke jihar ta Kaduna.

 

A cewar DCP Frank Mba mutumin ya amsa da bakin sa cewa shi mai satar mutane yana garkuwa da su ne, kuma shine ya kashe basaraken kasar ta Adara Maiwada Galadima

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!