Connect with us

Labarai

Kano: Ƴan sanda sun kama matasa 21 bisa yunkurin tayar da tarzoma yayin Maukibi

Published

on

Rundunar ƴan Sandan Jihar Kano ta ce, ta kama mutum 21 da ake zargi da yunkurin tayar da tarzoma yayin bikin Maukibi da aka gudanar cikin lumana.

Jami’an tsaro sun gano makamai masu hatsari da miyagun ƙwayoyi daga hannunsu, abin da ya taimaka wajen kare rayuka da tabbatar da tsaro.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ta rawaito Kwamishinan ƴan Sanda, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce, wannan nasara ta samo asali ne daga dabarun tsaro na zamani da haɗin gwiwa da sauran hukumomi da shugabannin al’umma ke bayarwa.

Ya kuma yaba da yadda jama’a suka gudanar da bikin cikin kwanciyar hankali.

Haka kuma, rundunar, ta buƙaci al’umma da su ci gaba da ba da hadin kai ga  rundunar yan sanda ta hanyar sanar da duk wani motsi ko mutum da ake zargi domin tabbatar da zaman lafiya a jihar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!