Connect with us

Addini

Kano: Hukumar Shari’a ta ƙaddamar da kwamitoci 80

Published

on

Hukumar Shari’a ta jihar Kano, ta ƙaddamar da kwamitoci guda Takwas, na malamai waɗanda za su rinƙa ziyartar hukumomi da makarantu da kuma kasuwanni, da sauran wurare, domin faɗakar da al’umma a ɓangarori daban-daban.

 

Kwamitocin sun haɗar da kwamitin da zai rinƙa zuwa hedikwatar Ƴan sandan Kano, da na Kasuwanni, da makarantu, da kuma na tashoshin Mota, da gidajen gyaran hali, da dai sauransu, domin faɗakar da al’umma, da ma mazauna gidaje, da makarantun.

 

Shugaban hukumar Sheikh Abbas Abubakar Daneji, ne ya jagoranci ƙaddamar da kwamitocin a jiya Litinin a ofishin hukumar, inda ya ce kafa kwamitocin ya biyo bayan yadda suka lura da buƙatar hakan, bisa  ziyarar da hukumar ta kai hukumomi da kuma gidajen a baya, inda shugabannin wuraren suka bukaci hakan domin faɗakarwa, da ilimantar da al’umma.

 

Sheikh Abbas Daneji, ya kuma buƙaci kwamitocin da su tsaya tsayin daka wajen gudanar da aiki yadda ya kamata, domin faɗakar da al’umma, da wa’azantar wa, tare da gyaran tarbiyya a matakai daban-daban.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!