Connect with us

Labarai

Kano: Kwamishina ya janye daga yin belin wanda ake zargi da siyar da ƙwayoyi 

Published

on

Kwamishinan Sufuri na jihar Kano, Alhaji Ibrahim Namadi, ya janye daga yunƙurinsa na karɓar belin wani da ake zargi da laifin dillalancin miyagun ƙwayoyi Suleiman Danwawu, a wata shari’ar da ake yi a gaban babbar kotun tarayya da ke Kano.

Shari’ar tsakanin gwamnatin Tarayya da Sulaiman Aminu mai lamba (FHC/KN/CR/93/2025), ta shafi zargin aikata laifukan da suka shafi muggan kwayoyi.

Rahotonni sun bayyana cewa, a baya Kwamishina Ibrahim Namadi ya tsaya a matsayin wanda zai tsaya wa wanda ake tuhuma.

Sai dai a daren yau Juma’a ne Ibrahim Namadi ya sanar da janye kansa daga karɓar belin ta cikin wata wasika da ya miƙa wa mataimakin magatakardar kotun.

A cikin wasikar, Kwamishinan ya kawo dalilai na ƙashin kansa, tare da buƙatar kare mutuncinsa da kuma kare martabar ofishinsa a matsayinsa na jami’in gwamnati.

Haka kuma, ya bayyana cewa ya yanke shawarar fara zama a matsayin wanda zai tsaya masa ne bisa ga ra’ayinsa, saboda alaka ta iyali da ta dade da kuma kula da jin kai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!