Connect with us

Labarai

Kano: Matashi ya rasu sakamakon nutsewa a Kududdufi

Published

on

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, tabbatar da mutuwar wani matashi mai suna Sulaiman Nura Ado, mai kimanin shekaru 14, sakamakon nutsewar da ya yi a cikin wani kududdufi  da ake kira da Ruwan Promise da ke unguwar Rijiyar Zaki.

Ta cikin wani sakon murya da ya fitar ga manema labarai, mai magana da yawun hukumar, ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce, sun samu kiran gaggawa ne bayan afkuwar lamarin.

Ya ce, jami’an hukumar sun samu nasarra ciro matashin daga cikin ruwan kafin rasuwarsa.

ACFO Saminu Yusif Abdullahi, ya ce, iftila’in ya faru ne a karshen makon da mu ka yi bankwana da shi.

Hukumar ta bukaci iyaye da sauran al’umma da su guji barin yara su na yin wanka a irin wadannan kududdufai domin kauce wa irin wannan iftila’i.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!