Connect with us

Labarai

Tattalin arzikin Najeriya ya fara farfadowa daga matsalolin da ya fuskanta

Published

on

Ministan Kuɗi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Wale Edun, ya bayyana cewa tattalin arzikin Najeriya, ya fara farfadowa daga matsalolin da ya fuskanta a baya.

Wale Edun, ya ce, lokacin da shugaba Bola Tinubu, ya hau mulki a 2023, tattalin arzikin na gab da durƙushewa, amma yanzu an samu ci gaba, inda ma’aunin tattalin arzikin kasa na GDP ya ƙaru da kashi 4.23 cikin ɗari, hauhawar farashin kaya ta sauka zuwa 18.02 cikin ɗari.

Ya kara da cewa darajar naira ta ƙaru zuwa N1,457 kan kowace Dalar Amurka, kuma farashin abinci kamar buhun shinkafa ya sauka daga N120,000 zuwa kusan N80,000. 

Ministan ya kuma amince cewa har yanzu akwai ƙalubale, musamman wajen biyan bashin ƙasa da ƙarancin kuɗin shiga, amma ya ce, sabuwar dokar haraji da sauran matakan da gwamnati ke ɗauka za su ƙara ƙarfin tattalin arzikin.

Haka kuma, Ministan, ya kara da cewa burin gwamnatin shugaba Tinubu shi ne kai ci gaban tattalin arziki zuwa kashi bakwai cikin ɗari nan da shekarar 2027.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!