Connect with us

Labarai

Kano: Rundunar yan sanda ta gargadi masu bai wa yara baburan Adaidaita Sahu

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano, ta gargadi mamallaka baburan Adaidaita sahu kan su guje wa bai wa kananan yara baburan suna hawa kan titunan jihar tare da gudanar da sana’a da su.

 

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan SP Abdullahi Hauna Kiyawa, ne ya bayyana hakan A daren Litinin din makon nan.

 

SP Kiyawa, ya ce, a cikin watannan da muke ciki na Agusta kadai yaran da ke tuka irin wadannan babura na Adaidaita sahu sun haddasa hadura har guda goma sha shida.

 

Ya yara da cewa, rundunar ta shirya tsaf don ganin ta cafke tare da gurfanar da duk wanda aka samu da aikata wannan laifi.

 

Haka kuma ya gargadi masu tukin ganganci da kuma masu kin bin dokar fitilar bada hannu da su guji yin hakan ko kuma su fuskanci fushin hukuma.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!