Labarai
Kano: Yara 2 sun rasu sakamakon nutsewa a kududdufi garin Najauro

Wasu yara biyu sun rasu sakamakon nutsewa a wani kududdufi da ke yankin Najauro a Karamar Hukumar Dawakin Kudu ta jihar Kano.
Rahotonni sun ruwaito cewa, lamarin ya faru ne a wani kududdufi da ke kofar arewa kan hanyar zuwa babban asibitin Dawakin Kudu yayin da yaran suka je domin yin wanka inda suka nutse a ciki.
Al’ummar unguwar sun yi kokarin lalubo gawarwakin yaran, inda aka samu daya nan take.
An kuma ɗauki lokaci kafin a samo dayan, da taimakon ɗan gidan Sarkin Ruwa mai suna Dan Babiyo Jarmai inda aka samu nasarar fito da gawar daya yaron.
Yaran da suka rasu sun hada da Naziru Saleh mai shekaru 11 da Mubasshir Sani mai shekaru 12.
Tuni aka yi jana’izarsu kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.
You must be logged in to post a comment Login