Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar Shanono ta bukaci gwamnati ta gyara Dam ɗin yankin tare da gina wani sabo

Published

on

Shugaban karamar hukumar Shanono, Alhaji Abubakar Barau, ya bukaci gwamnatin jihar Kano da ta gina sabon Dam a garin Dutse da kuma gyara Dam ɗin Shanono, domin sauƙaƙa matsalar ruwa da ake fama da ita a yankin.

 

Abubakar Barau, Ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin Kwamishinan ma’aikatar raya karkara Dakta Abdulkadir Abdussalam, a ofishinsa, inda ya ce, al’ummar ƙaramar hukumar na matukar  shan wahala wajen samun ruwan da za su yi amfani da shi.

 

A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da jama’a na ma’aikatar, Faruk Ghali Masanawa ya fitar, shugaban ƙaramar hukumar ya gode wa gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, da Kwamishinan raya karkara bisa ziyarar da suka kai domin jin koken jama’a a karkara.

 

Kwamishina Abdussalam, wanda ya samu wakilcin Babban Sakataren ma’aikatar, Alhaji Musbahu Ahmad Badawi, ya ce, ziyarar na cikin matakin tattara bayanai domin samar da ababen more rayuwa a kananan hukumomi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!