Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisar dokokin ta bukaci gwamntin jida da ta kawo wa al’ummar Alajawa a Shanono dauki

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jiha da ta kai daukin gaggawa ga al’ummomin da ke mazabar Alajawa a yankin karamar hukumar Shanono sakamakon barnar da ruwan sama kamar da bakin kwarya ta yi musu.

Hakan ya biyo bayan kudirin gaggawa da dan majalisa mai wakiltar mazabar Bagwai da Shanono Ali Ibrahim Isah Shanono ya gabatar yayin zaman majalisar na jiya.

Da ya ke zantawa da manema labarai bayan zaman majalisar Ali Ibrahim Shanono wanda shine shugaban kwamitin kula da ilimi mai zurfi na majalisar, ya ce; ruwan da aka yi a makon jiya yayi matukar barna ga jama’ar yankin.

A wani labarin kuma kungiyar Kanawa educational foundation for disable ta yi kira ga gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da ya gaggauta sanya hannu kan dokar masu bukata ta musamman da majalisar dokokin jihar Kano ta sahalewa a jiya.

Shugaban kungiyar Abba Sarki Sharada ne ya bayyana haka ga manema labarai a farfajiyar majalisar dokokin jihar Kano a jiya.

Wakilin mu Abdullahi Isah ya ruwaito shugaban majalisar dokokin na Kano Yusuf Abdullahi Ata na cewa, da zaran dokar ta fara aiki za ta taimaka gaya wajen kyautata rayuwar mutane masu bukata ta musamman

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!