Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Karo Na Biyu:Gwamnan Kano Abba Gida-Gida ya ƙaddamar da rabon kayan Abinci

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta ƙaddamar da rabon kayan abinci karo na biyu ga al’ummar jihar na ƙananan hukumomi 44, inda gwamnatin ta ce zata fara rabawa al’ummar kano ta tsakiya adadin buhhuna 105600 da suka haɗar da shinkafa da masara

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ne ya tabbatar da hakan a yau yayin taron ƙaddamar da rabon kayan abinci ga al’umma jihar Kano domin rage matsin rayuwa da al’umma suke ciki

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma ce zasu kasance masu saka ido wajen ganin kayan sun isa ga mabuƙatu a dukkanin ƙananan hukumomi kano

Gwamnan ya kuma ƙara da cewa sunyi tsarin zuwa gidan marayu da gajiyayyu da sauran guraren da su ke a killace domin basu nasu kayan abincin

Haka kuma gwamnan ya ce suma dukkan wani nau’i na jami’an tsaro da ƴan jarida suma akwai wani tsari da akayi musu wajen suma wannan kayan abincin sun isa gare su

A karo na biyu gwamnatin zata raba sama da buhhuna sama da dubu ɗari a wannan lokaci inda tace zata ci gaba da samarwa da al’ummar jihar hanyoyin samar musu da saukin rayuwa

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!