Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Kasar Spain ta gayyaci ‘Adama Traore’ cikin tawagar ‘yan wasanta

Published

on

Daga Anas  Muhammad Mande

Kasar Spain ta gayyaci dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Wolverhampton Wanderers da ke kasar Ingila Adama Traore, da ya shiga cikin tawagar ‘yan wasanta a karawar da kasar za ta yi da kasar Jamus da kuma Ukraine.

Adama Traore mai shekara 24, a watan Janairun da ya gabata, ya bayyana cewa kawo yanzu bai yanke shawara kowace kasa zai wakilta ba tsakanin kasar ta Spain da kuma kasar sa ta asali Mali.

A kwanakin baya Spain ta gayyaci Adama Traore don wakiltar ta a fafatawar su da kasar Romania a watan Nuwamban shekarar da ta gabata, amma bai samu ikon amsa gayyatar ba sakamakon raunin da ya yi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!