Labaran Kano
Kasar Spain ta gayyaci ‘Adama Traore’ cikin tawagar ‘yan wasanta
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/08/adama-tour-50ce82b9-7be3-4eee-9695-f3ea842c14f-resize-750.jpg)
Daga Anas Muhammad Mande
Kasar Spain ta gayyaci dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Wolverhampton Wanderers da ke kasar Ingila Adama Traore, da ya shiga cikin tawagar ‘yan wasanta a karawar da kasar za ta yi da kasar Jamus da kuma Ukraine.
Adama Traore mai shekara 24, a watan Janairun da ya gabata, ya bayyana cewa kawo yanzu bai yanke shawara kowace kasa zai wakilta ba tsakanin kasar ta Spain da kuma kasar sa ta asali Mali.
A kwanakin baya Spain ta gayyaci Adama Traore don wakiltar ta a fafatawar su da kasar Romania a watan Nuwamban shekarar da ta gabata, amma bai samu ikon amsa gayyatar ba sakamakon raunin da ya yi.
You must be logged in to post a comment Login