Connect with us

Labarai

kasashe Afrika 16 na fama da karancin abinci-Majalisar dinkin duniya

Published

on

Hukumar samar da abinci da kayayykin noma na majalisar Dinkin Duniya ta ce kasashe goma sha shida na fama da karancin abinci a fadin duniya, ciki har kasashen Afrika.

Hukumar ta ce kasashen da abun ya shafa sun hada da Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo da Burundi da Liberia da Mali da Somalia da Sudan ta kudu da kuma Sudan.

Sauran kasahen sune Guinea-Bissau da Haiti da Iraq da Afganistan da Lebanon da Syria da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya da Ukraine da Burundi da kuma kasar Yemen.

Hukumar ta ce yawaitar rikice-rikece da ake samu a kasashen shi ne umul-abaisin samun karancin abinci ga al’ummar kasashen.

A cewar ta, kasashen Yeman da Sudan ta kudu da Syria da Lebanon da Ukraine da Afganistan da kuma kasar Somalia sun samun karancin abinci.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!