Connect with us

Labarai

Kashim Shettima zai jagoranci tawagar gwamnatin tarayya zuwa jajanta wa ‘yan kasuwar Singa

Published

on

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, zai jagoranci tawagar gwamnatin tarayya zuwa jihar Kano domin jajanta wa ‘yan kasuwar da gobara ta shafa a kasuwar Singer.

 

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ne ya ba shi wannan umarni, inda tawagar za ta tashi daga Abuja gobe domin isar da sakon jaje ga ‘yan kasuwar da suka yi asarar biliyoyin naira sakamakon gobarar da ta tashi a karshen mako karo na biyu cikin makonni biyu.

 

Gwamnatin tarayya ta ce za ta kuma yi alkawarin tallafin kudi domin taimaka wa wadanda abin ya shafa tare da taimakawa jihar Kano wajen gaggauta bude kasuwar.

 

Daga cikin tawagar akwai Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas; Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin; Sanata Kawu Ismaila; da kuma shugaban kwamitin kasafin kudi na Majalisar Wakilai, Abubakar Kabir Bichi.

 

Haka kuma Ministan Harkokin Jin Kai, Bernard M. Doro, da Darakta-Janar ta NEMA, Zubaida Umar, na cikin tawagar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!