Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Ƴan majalisa na duba ayyukan gwamnatin tarayya a Kano

Published

on

Mambobin kwamitin ayyuka na majalisar wakilai ta tarrayya sun kai ziyara fadar gwamnatin Kano.

Shugaban kwamitin Abubakar Kabir Bichi ya ce sun kai ziyarar ne a wani ɓangare na zuwan su Kano tare da tawagar sa domin duba ayyukan hanyoyin da gwamnatin tarayya ke yi duba da muhimmancin su ga al’umma.

Ya ƙara da cewa, ayyukan da suka zo dubawa sun haɗa da aikin hanyar da ya tashi daga Abuja, Kaduna, Zariya, zuwa Kano, tare da hanyar Kano zuwa Maiduguri, da sauransu.

Kabir Bichi ya ce, zasu tabbatar ƴan kwangilar sun kammala ayyukan cikin lokacin da aka ɗibar wa aikin da kuma tuntuɓar su kan matsalolin da suke fuskanta domin magance su.

Da yake jawabi yayin karɓar su gwamna Dr Abdullahi Umar Ganduje ya gode musu bisa ga wannan ƙoƙari, inda yace hakan zai taimaka wajen rage rasa rayuka da akeyi a manyan hanyoyin.

Wakiliyar mu Zahra’u Nasir ta rawaito cewa gwamnan ya nemi ƴan kwamitin da su ja hankalin ƴan kwangilar wajen dagewa a kan ayyukan su sakamakon yanayin damina da ake ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!