Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kaso daya cikin dari ke samun gurbin karatu a jami’oin kasar nan

Published

on

Hukumar kula da jami’oi ta kasa NUC, ta ce; kaso daya cikin dari na adadin al’ummar kasar nan ne kawai suka iya samun gurbi a jami’oin kasar nan guda dari da sittin da hudu.

 

Shugaban hukumar ta NUC farfesa Abubakar Rashid ne ya bayyana haka, yayin zantawa da manema labarai jiya a Abuja.

 

Ya ce, jami’oi masu zaman kansu guda saba’in da biyar da kasar nan ke da ita, sun iya daukar kaso biyar da digo talatin da daya cikin dari ne kacal na daliban da ke jami’oin kasar nan.

 

Farfesa Abubakar Rashid, ya kuma bukaci da a kara adadin jami’oin tare da bude sababbi.

 

Shugaban hukumar ta NUC, ya ce; akwai damuwa matuka ganin cewa a yanzu adadin daliban da suka samu gurbi a jami’oin kasar nan su miliyan daya da dubu dari tara da sittin da daya ne kacal.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!