Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Hukumar WAEC ta saki sakamakon jarrabawar watan Mayu da Yuni

Published

on

Hukumar WAEC da ke shirya jarrabawar kammala karatun sakandire ta yammacin Afurka, ta saki sakamakon jarrabawar bana na watan Mayu da Yuni.

Da yake sanar da sakin sakamakon, shugaban hukumar mai kula da kasar nan Mr. Olu Adenipekun, ya ce cikin dalibai miliyan daya da dubu dari biyar da saba’in da biyu da su ka rubuta jarrabawar a bana, dubu dari bakwai da tamanin da shida da goma sha shida sun samu sakamako mai kyau wato credit biyar zuwa sama ciki kuwa har da darusan lissafi da turanci.

Ya kuma shawarci wadanda suka rubuta jarrabawar kuma suka tabbatar da cewa sun biya kudin su lakadan, da su ziyarci shafin hukumar a yanar gizo domin duba sakamakon su.

A cewar sa sakamakon na bana, ya nuna cewa kaso arba’in da tara da digo casa’in d takwas sun samu sakamako mai kyau

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!