Connect with us

Labarai

Katsina: Yan sanda ta umarci jami’anta su bai wa makarantu tsaro

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ta umarci jami’anta da su bai wa dukkanin makarantun jihar tsaron da ya kamata.

Hakan na cikin wata sanarwa da jami’in yada labaran rundunar a jihar DSP Abubakar Aliyu ya fitar a safiyar yau.

Sanarwar ta kuma ce kwamishinan yan sandan jihar Bello Shehu, ya ce umarnin na zuwa ne yayin wani zaman tattaunawa da rundunar ta gudanar kan yadda ake samun matsalolin sace dalibai a kasar nan.

Ya kuma ce hakan na zuwa ne kan umarnin da babban sefeton yan sandan kasar nan Kayode Egbetokun, ya bayar kan bayar da tsaron da ya kamata a makarantun kasar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!