Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kawu Sumaila: kafafun yada labarai abokan tafiyar mulkin dumukaradiyya ne

Published

on

Tsohon mai taimakawa Shugaban kasa Muhammadu Buhari kan al’amuran majalisar wakilai ta kasa Kawu Sumaila ya bayyana kafafun yada labarai a matsayin abokan tafiyar da mulkin dumukaradiyya ako ina a Duniya.

Kawu Sumaila ya bayyana hakan ne yayin gudanar da rantsuwar sabbin shuwagabannin kungiyar wakilan kafafen yada labarai reshan jihar Kano wanda aka gudanar a yau Alhamis.

Kawu Sumaila, wanda ya kasance shugaban taron ya kuma kara da cewa ta hayar tsayayyar kafar yada labarai ne kadai za’a iya tabbatar da mulkin dumukaradiyya a kowacce kasa a duniya.

da yake gabatar da nasa jawabin, sabon shugaban kungiyar wakilan kafafen yada labarai reshan jihar Kano, Kwamared Ibrahim Garba Shu’aibu, ya ce a lokacin mulkinsa zai tabbatar da walwalar ‘ya ‘yan kungiyar tare da samar musu yanayin aiki mai kyau.

kungiyar ta wakilan kafafen yada labaran sun zabi Ibrahim Garba a matsayin Shugaba da Mustapha Hodi a matsayin sakatare da sauran su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!