Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Kwamitin da ke binciken zargin fitar da biliyan 33 daga asusun hukumar kula da fansho zai gabatar da rahoton sa

Published

on

Kwamitin wucin gadi na majalisar wakilai da ke binciken zargin fitar da naira biliyan talatin da uku daga asusun hukumar kula da fansho ta kasa zai gabatar da sakamakon rahoton sa a makon gobe.

Shugaban kwamnitin Benjemin Wayo ne ya bayyana hakan jiya Alhamis yayin zantawa da manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Ya ce burin kwamitin shi ne kawo gyara a harkokin fanshon Najeriya, a don haka ta yi cikakken bincike domin gano gaskiyar lamarin.

Haka haka masu binciken sun bukaci masu ruwa da tsaki da al’ummar Najeriya nan da cewa, idan suna da wani bayani da zai taimakawa kwamitin kan hukumar ta ‘yan fansho ta kasa da su rubuta wa kwamitin nan da kwanaki hudu masu zuwa.

Ya kuma ce kwamitin zai shawarci gwamnati da ta karbi bayanan da al’umma suka shigar gaban ta saboda hakan zai taimaka wajen binciken.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!