Connect with us

Labarai

Kebbi: Yan sanda sun kashe ƴan bindiga 3 tare da ƙwato bindiga da harsasai

Published

on

Rundunar ƴan sandan jihar Kebbi ta ce, jami’anta sun samu nasarar kashe wasu ƴan bindiga uku, tare da ƙwato bindiga ƙirar AK47 da harsasai da dama a yankin ƙaramar hukumar Shange da ke jihar.

 

Jaridar Daily Trust ta ruwaito kakakin rundunar, CSP Nafiu Abubakar, rundunar ta ce ƴansanda sun fafata da ƴanbindigar ne a yankin na Shanga tare da taimakon ƴan-sa-kai, sannan wasu sun tsere da raunuka.

 

Kakakin ya ƙara da cewa wasu ƴanbindigar sun kai hari a garin Kesan da ke Shanga ɗin dai, inda suka yi garkuwa da mutum ɗaya mai suna Abdulmumini Alhaji Ahmadu mai shekara 25.

 

Ya ce, amma daga bisani ƴansandan sun bi ƴanbindigar, inda suka samu nasarar ceto mutumin, amma sun harbe shi a ƙafa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!