Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kimanin yan cira ni 200 ake tsammanin sun mutu a tekun Baharrum

Published

on

Hukumar kula da ‘yan-cirani ta duniya ta ce wasu bakin haure ‘yan afurka sama da dari biyu ake tsammanin sun mutu a tekun Baharrum.

 

A cewar hukumar ta IOM ‘yan-ciranin wadanda ake tsammanin mafi yawansu ‘yan kasar nan ne suna kan hanyar su ne ta zuwa kasashen Italiya da Spaniya.

 

Babban jami’in yada labaran hukumar a kasar Libya Christine Petre, ta ce jiragen kwale-kwalen da suka nutse a tekun sun bar gabar ruwan Azzawiyah da Alkhums da ke kasar Libya ne zuwa kasashen turai.

 

Jami’an tsaro da ke gadin gabar tekun kasar Libya sun bayyana cewa sun samu nasarar ceto wasu daga cikin ‘yan ciranin wadanda kuma sun fito ne daga kasashen Senegal da Nigeria da kuma Mali, yayin da kuma akwai wasu guda takwas da suka fito daga kasar Bangladesh sai kuma wasu biyu ‘yan kasar Pakistan.

 

Rahoton na hadin gwiwa da hukumar kula da ‘yan cirani ta duniya da jami’an tsaro masu gadin gabar tekun Libya suka fitar, sun ce; har I zuwa yanzu akwai wasu mutanen sama da dari biyu da har yanzu ba akai ga gano inda su ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!