Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

kotu ta aika wa shugaba Buhari da Atiku takardar sammaci

Published

on

Wata babbar kotun tarayya a Abuja ta aike da takardar sammaci ga shugaban kasa Muhammadu Buhari da kuma Atiku Abubakar bisa zarigin su da barnatar da kudin da ya haura naira biliyan daya lokacin yakin neman zabe.

Cikin kunshin karar da dan takardar jam’iyyar NRM Usman Ibrahim Alhaji ya shigar gaban kotun ya nemi da a soke zaben shugaban kasar da aka gudanar a ranar 23 ga watan Fabrairun da ya gabata.

Usman Ibrahim ya bukaci kotun da ta yi amfani da sashe na 91 (2) na kundin dokokin hukumar zabe na shekarar 2010.

Ya kuma ce akwai bukatar kotun da soke Buhari da Atiku da shiga cikin takarar saboda sun yi amfani da sama dai naira biliyan guda kowanne su yayin yakin neman zaben.

Haka kuma ya kara da cewa yana fata kotun za ta yi abin da ya da ce wajen aikewa da wadanda ake tuhumar takardar karar su kuma amsa gayyatar kotun, domin tuhumar su kan laifukan da suka aikata.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!