Connect with us

Labarai

Kotu ta ba da umarnin kama babbar sakatariyar hukumar ƙasa da safiyo ta jihar Kano

Published

on

Wata babbar kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a kofar kudu anan birnin Kano, ta umarci kwamishinan ƴan sandan jihar Kano da ya kamo mata babbar sakatariya a hukumar kula da ƙasa da safiyo, Dr. Zainab Yusuf Buraje, sakamakon bijirewa umarnin Kotu.

 

Kotun karkashin jagorancin mai shari’a Ibrahim Sarki Yola, ta ce, babbar sakatariyar, Dr Zainab Yusuf Buraje, ta ki bin umarnin kotu wadda ta bukace ta, da ta ba da wata takardar shaida da ake shari’a, akanta.

 

A cewar alkalin kotun, duk da an turawa babbar sakatariyar da rubutacciyar wasika da ke neman bayani kan takardar shaidar, amma ba ta bi umarnin da kotun ta ba ta ba, saboda haka, ya umarci kwamishinan ƴan sandan Kano da ya kamata ya gabatar da ita gaban kotun, cikin mako ɗaya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!