Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yanzu-yanzu: Kotu ta dakatar da Anti-Corruption daga bincikar Sarkin Kano

Published

on

Babbar kotun tarayya dake Kano karkashin mai shari’a lewis Alagua ta dakatar da hukumar karbar korafe-korafe ta jihar Kano da shugaban ta Muhyi Magaji Rimingado daga binciken sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi na biyu.

Cikin kunshin umarnin wanda sarkin Kano ya shigar da karar Muhuyi da hukumarsa da kwamishinan Shari’a da gwamnan Kano, Mai shari’a Alagua ya ayyana cewar kowa ya tsaya a matsayarsa yanzu magana ta dawo kotu.

Wakilinmu yusuf Nadabo Ismail ya ruwaito cewar Mai shari’a Alagua ya sanya ranar 18 mayu dan kowane bangare ya gabatar da jawabansa.

Hukumar karbar korafe-korafe ta gayyaci sarkin cewar ya bayyana a gabanta domin amsa wasu tambayoyi dangane da wasu zarge-zarge a ranar litinin mai zuwa.

Kodayake yanzu maganar ta koma kotu.

Ko a watan da ya gabata ma babbar kotun tarayya mai lamba biyu ta soke wani bincike da hukumar tayi inda kotun ta ayyana cewar an tauyewa sarkin yancin da kundin tsarin mulkin kasa ya bashi.

Ku kalli takardar koton a kasa:

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!