Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta ci tarar hukumar KAROTA kan kama wasu da ta yi saboda sun yi goyo a babur

Published

on

Babbar kotun jiha mai Lanba 14 ƙarkashin mai shari’a Nasir Saminu ta yanke hukunci dangane da shari’ar da wasu mutane uku suka shigar da suke kalubalantar hukumar KAROTA na kamasu da ta yi yayin da suka yi goyo a babur kuma aka ci tararsu.

A zaman kotun na ranar Litinin mai shari’a yayi karatun baya inda daga karshe kotun ta haramta kamen goyon da KAROTA ta yi musu, da kuma yankewa mutane tarar tunda ba baburin haya ba ne.

Kotun kuma ta umarci hukumar KAROTA da ta biya wadanda suka yi karar su uku Bello Basi Fagge da Lamin Ibrahim Adam da kuma Ibrahim Abdullahi za ta biyasu Naira dubu dari biyar biyar kowannensu.

Haka kuma za ta biyasu kudin kara Nairar dubu dari da kuma kudin da akaci tararsu Naira dubu bibiyu, kamar yadda wakilin Freedom Radiyo Aminu Abdu Baka Noma ya rawaito.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!