Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kotu ta gayyaci Diezani Alison-Madueke

Published

on

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci tsohuwar ministar man fetur na kasar nan Diezani Alison-Madueke da ta gurfana gabanta don kare kanta kan zargin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ke yi mata na halasta kudin haramun.

Alkalin kotun mai shari’a Ijeoma Ojukwu ce ta ba da umarnin bayan da lauyan EFCC Faruk Abdallah ya bukaci hakan.

Mai shari’a Ijeoma Ojukwu dai ta bukaci Diezani Alison-Madueke wadda ta tsere daga kasar nan bayan da ta sauka daga mukaminta a shekarar dubu biyu da goma sha biyar zuwa kasar Burtaniya, da ta gurfana gaban kotun don kare kanta kan tuhume-tuhume guda goma sha uku da hukumar EFCC ke yi akanta.

Wasu daga cikin zarge-zargen da hukumar ta EFCC ke yi ga tsohuwar ministar sun hada da: haramta kudaden haramun naira biliyan goma sha hudu da miliyan ashirin da tara da kuma wasu kudade naira biliyan uku da miliyan talatin da biyu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!