Connect with us

Labarai

Kotun koli ta jaddada matakin da INEC ta dauka na soke lasisin wasu jam’iyyu 74

Published

on

Kotun Kolin kasar nan karkashin Justice Adamu Jauro, ta jaddada hukuncin da Kotun daukaka kara ta zartar na soke rajistar jam’iyyun siyasa 74 a Najeriya.

 

A bara ne dai hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta soke rajistar jam’iyyun sakamakon gaza samun nasarar lashe ko da zabe guda daya a babban zaben shekarar 2019, kamar yadda doka ta yi tanadi.

 

A ranar 29 ga watan Yulin bara ne dai Kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da cewa matakin INEC na rushe jam’iyyun yana bisa ka’ida.

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!