Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kudirin dokar neman rushe hukumar NYSC ya tsallake karatu na farko

Published

on

Kudirin dokar neman rushe hukumar kula da masu yiwa kasa hidima ya tsallake karatu na farko a zauren majalisar wakilai a yau Litinin.

Dan majalisa Awali Inombek Abiante shine ya dauki nauyin kudirin wanda ya bayyana dalilai da dama da ya ce ya kamata a rushe hukumar ta NYSC.

Kudirin dokar na neman gyara sashe na dari uku da goma sha biyar, biyar cikin baka A cikin baka na kundin tsarin mulkin kasar nan na 1999.

A cewar sa, ci gaba da kashe-kashen ‘yan hidimar kasa a sassa daban-daban na kasar nan da ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda ke yi, ba ya ga rikicin kabilanci da na addini, shi ya sanya ya ga dacewar rushe aikin na hidimar kasa baki daya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!