Connect with us

Labarai

Alarammomin tsangaya sun koka kan rashin ganin Malaman da gwamnatin Kano ta aika musu

Published

on

Kungiyar Alarammomin tsangaya sun koka kan rashin ganin Malaman da gwamnatin Kano ta tura makarantun tsangaya dan koyar da Almajirai ilimin Zamani.

A cewar Malaman tsangayar malaman da aka turo sun  daina zuwa makarantun  ba tare da sanar dasu dalilin yin hakan ba.

Tsarin wanda gwamnatin ta  dauki malaman sakai 600 tare da biyan su alawus dan koyawa yara almajrai ilimin lissafi da turanci a wasu makarantu  fiye da 300 a kanan hukumi 44 na jihar Kano.

Sai dai  Malaman tsangayar sunce tun bayan fara wannan shiri malaman da gwamnatin ta tura suka dai na zuwa mafi yawan makarantun da aka tura su.

Alaramma malam Yusuf Wanda aka fi sani da malam babba guda ne daga cikin malaman tsangaya a nan Kano ya ce daliban nasa sun fara gane darasin da aka fara koya musu kwatsam sai  malamin ya daina zuwa.

A  shekarar 2019 ne gwamnatin Kano  ta bullo da shirin  shigar da Almajirai na Tsangaya tsarin Karatun , mai taken integrated system of almajiri education a wani mataki na inganta tsarin harkar makarantun tsangaya.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!