Labarai
Kungiyar Amnesty ta koka kan DSS da ke kama mutane game da yakin Iran

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International ta nuna damuwa kan abin da ta kira kara tsaurara mataki da Hukumar farin kaya ta DSS ke yi kan masu yin sharhi a kafofin sada zumunta game da yakin Gabas ta Tsakiya.
Kungiyar ta ce akalla mutane biyu mazauna Kaduna an tsare su, kuma ana shirin gurfanar da daya daga cikinsu a kotu bisa tuhume-tuhumen da ta kira marasa tushe.
A cewar kungiyar, sukar manufofin gwamnatocin Amurka ko Isra’ila hakki ne na ‘yancin fadin albarkacin baki da kundin tsarin mulkin Nijeriya na 1999 ya tanada, don haka ta bukaci hukumomin kasar su mutunta wannan hakki ba tare da tsoratar da masu ra’ayi ba.
You must be logged in to post a comment Login