Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Matsin rayuwa: DSS ta hana NLC yin zanga-zanga

Published

on

Hukumar tsaron farin kaya DSS ta yi kira ga ƙungiyar ƙwadago NLC da ta janye ƙudurinta na shirya zanga-zangar gama gari domin samun zaman lafiya a Najeriya.

Ƙungiyar NLC ta sanar da fara yajin aikin a ranar 27 da 28 ga watan Fabarairu domin nuna rashin jin daɗinta kan halin matsin rayuwa da al’umma ke ciki a ƴan Najeriya.

Wannan na zuwa ne yayin da kwamishinan ƴan sanda a Abuja Ben Igweh cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta fitar, yana mai cewa rundunarsa ba ta da masaniya kan zanga-zangar da ake shirin yi a Abuja.

Sanarwar ta DSS ɗauke da sa hannun Daraktan yaɗa labarai na hukumar, Dakta Peter Afunanya, ta ce DSS ta samu labarin akwai wasu mutane da ke shirin yin amfani da zanga-zangar wajen tayar da husuma da kuma rikici.

DSS ta kuma yi kira ga ƙungiyoyin su tattauna a maimakon yin abin da ka iya tayar da hankali.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!