Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Kungiyar malaman kwalejojin kimiyya da fasaha ta yi barazanar tsunduma yajin aiki

Published

on

Kungiyar malaman kwalejojin kimiyya da fasaha ta kasa (ASUP) ta yi barazanar shiga yajin aiki, matukar gwamnatin tarayya ta kyale hukumar kula da ilimin sana’a ta kasa (NBTE), ta ci gaba da cin zarafin ma’aikatan ta, ta cikin shirin biyan albashin ma’ikata na hadaka.

Haka kuma kungiyar ta zargi gwamnatin tarayya da rashin cika alkawari kan yarjejeniyar fahimtar juna da suka sanya wa hannu a shekarar da ta gabata.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kungiyar Usman Dutse.

Sanarwar ta ce kungiyar ba ta zabi da ya wuce ta tsunduma yajin aiki matukar wa’adin kwanaki 21 ya cika ba tare da daukar wani mataki kan lamarin ba.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!