Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Transparency international:akwai bukatar gudanar da binciken karbar na goro da ake zargin gwamnan Kano

Published

on

Kungiyar kasa da kasa da ke yaki da cin hanci da rashawa wato transparency international, ta bukaci da a gudanar da bincike da babu hannun gwamnati a ciki, kan zargin karbar na goro da ake yiwa gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje.

 

Shugaban kungiyar a nan Najeriya Auwal Musa Rafsanjani ne ya bayyana haka yayin zantawa da jaridar Solacebase a Abuja.

 

Ya ce gudanar da bincike ba tare da sanya bakin gwamnati ba, zai taimaka gaya wajen yaki da ake da cin hanci da rashawa a kasar nan.

 

Shugaban kungiyar ta Transparency International a nan Najeriya, ya kuma ce, kwamitin da majalisar dokokin Kano ta kafa kan batun, ba zai iya gudanar da aikin sa bisa gaskiya da adalci ba.

 

Kungiyar ta Transparency International ta bakin shugaban ta Auwal Musa Rafsanjani, ta kuma bukaci gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da ya sauka daga mukamin sa don gudun tsoma bakin sa a cikin binciken da ake yi a kansa.

 

A cewar kungiyar ba zai yiwu gwamnan ya zama mai laifi kuma ya zamo alkali ba, saboda alakar sa da ‘yan majalisu, ba zai sa suyi aiki bisa gaskiya da adalci ba.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!