Connect with us

Labarai

Kwamitin Ma’aikatar Shari’a ya gano ƙarrakin da ke buƙatar kammala su da wuri

Published

on

Kwamitin da ma’aikatar shari’a ta kafa domin gano manyan shari’un da suka jima ba a kawo karshen su ba, ya gano wasu manyan shari’o’i da ke buƙatar a kammala su cikin gaggawa.

 

Kwamishinan Shari’a, Barista Abdulkarim Kabiru Maude SAN, ne ya kafa kwamatin don kawo karshen shari’un da aka dade ana yinsu, tare da rage cunkosan jama’a a gidajen gyaran hali.

 

Hakan na cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labaran ma’aikatar Najib Lawan Danbazau, ya fitar ga manema labarai.

 

Sanatwar ta ce, kwamatin mai mambobi 7 karkashin jagorancin Barista Rabi’at Sa’ad Sule, ya fara aikin sa da ziyartar kotunan majistare na Gyadi-Gyadi inda ya ziyarci kotuna 7 daga cikin goma sha biyar da ke yankin.

 

A yayin ziyarar, kwamitin ya gano wasu shari’o’in da suka dade ba a kawo karshen su ba, tare da bukatar sakeyin nazari a kansu.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa, yayin ziyarar shugabar kwamitin Barista Rabi’at Sa’ad Sule, ta yaba da jajircewar ma’aikatan kotu, tana mai cewa kwamitin na da nufin gano matsaloli da samar da mafita domin tabbatar da ingantaccen tsarin shari’a a jihar Kano.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!