Connect with us

Labarai

Kwastam za ta fara shiga kasuwanni da wuraren ajiye kaya domin kwato shinkafar kasar waje

Published

on

Babban jami’in hukumar yaki da fasakwauri ta kasa Kwastam mai kula da shiyya ta biyu wato zone B Albashir Hamisu ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da Jaridar Daily Trust.

“Ba za mu iya kawo karshen fasakwaurin shinkafa zuwa cikin kasar nan kwata kwata ba, amma muna iya kokarinmu wajen dakile safarar shinkafar” in ji Albashir Hamisu.

“Kuma mun kammala shiri tsaf don fara kai samame cikin kasuwanni da manyan wuraren ajiyar kayayyaki wato warehouses don kwato shinkafar kasar waje da aka shigo da ita kasar nan da ma sauran kayayyakin da aka haramta shigo da su Najeriya” a cewar Albashir Hamisu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!