Connect with us

Kiwon Lafiya

Likitocin Najeriya na shirin tsunduma yajin aiki a makon nan

Published

on

Kungiyar Likitocin Njeriya NMA ta ce, zuwa ranar Alhamis mai zuwa idan har gwamnatin tarayya ba ta cika mata alkawuran da ta dauka ba, to za ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

 

Shugaban kungiyar Farfesa Bala Audu, ne ya bayyana hakan a zantawar sa da Jaridar The Punch.

 

Ya kuma ce, kamar yadda gwamnatin ta yi wa kungiyar alkawari a zaman da suka gabatar a baya-bayan nan, kan za ta biya musu bukatun su kafin nan da ranar 23 ga watan da muke ciki na Yuli wanda zai kama ranar Alhamis din makon nan.

 

Shugaban kungiyar ta NMA ya kuma ce, suna yin hakan ne domin samar da gyara a fannin Lafiya da zai sa a samu yadda ake bukata wajen kula da lafiyar al’ummah.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!