Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Majalisa ta aikewa hukumar tattara haraji ta FIRS takardar tuhuma

Published

on

Majalisar dattijai

Majalisar dattijai ta aika da takardar tuhuma ga hukumar tattara haraji ta kasa FIRS, sakamakon zargin hukumar da kin sanya wasu kudade da ta karbo daga ma’aikatu da hukumomi da kuma sassan gwamnati a cikin asusun tarayya.

A cewar Majalisar kudaden dai sun kai naira tiriliyan daya da biliyan dari hudu.

Takardar tuhumar ta biyo bayan rahoton babban mai binciken kudi na tarayya na shekarar dubu biyu da goma sha biyar, wanda aka mika shi ga shugaban kwamitin sanata Mathew Urhoghide.

Kwamitin dai yana gudanar da bincike ne kan kudaden da hukumomin gwamnati suka kashe cikin shekaru biyar da suka gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!